✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

NDLEA ta kama matafiyin da ya boye Hodar Iblis a gabanshi

Mutumin dai ya hadiye kulli 40 ne na hodar a cikinsa

Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA) ta ce ta kama wani matafiyi da ya dawo daga kasar Brazil mai suna Igwedum Uche Benson, dauke da kulli-kullin Hodar Iblis din da ya boye a gabanshi.

Dubun mutumin ta cika ne a dakin saukar matafiya na filin jirgin sama na murtala Muhammad da ke Legas a ranar Litinin din da ta gabata.

An kama shi ne jim kadan da saukar shi a wani jirgin Ethiopian Airline wanda ya taso daga birnin Sao Paulo na Brazil, kuma ya ya da zango a Addis Ababa, babban birnin Habasha.

Kakakin NDLEA, Femi Babafemi ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa ranar Lahadi.

A cewar kakakin hukumar, bincikensu na farko-farko na nuni da cewa wanda ake zargin ya hadiye kulli 50 ne na hodar a cikinsa kafin ya tafi kasar ta Brazil.

Ya ce bayan Igwedum ya isa Addis Ababa ne ya kasayar da kulli 48, wanda ya mika su ga wani mutum a can.

Sai dai wanda ake zargin ya yi ikirarin cewa ya gaza kasayar da ragowar kulli biyun ne a dakin wani otal da ke Addis Ababa, sai daga bisani ya kasayar da su a bandakin jirgin da ya taso daga Addis Ababan zuwa Legas.