✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

NFF ta kori Eguavoen bayan gaza zuwa Gasar Kofin Duniya

NFF ta janye kwantaragin shekara biyu da ta bai wa Eguavoen

Hukumar Kwallon Kafa ta Najeriya (NFF), ta sallami kocin tawagar ’yan wasan Super Eagles Augustine Eguavoen da mukarrabansa, kwana biyu bayan gaza samun tikitin zuwa gasar Kofin Duniya ta 2022 a za a yi a Qatar.

Sakatare-Janar na hukumar, Dokta Mohammed Sanusi ne, ya bayyana haka cikin wata sanarwa, inda ya ce hukumar ta janye kwantaragin shekara biyu da ta bai wa Eguavoen.

“Biyo bayan gaza zuwa gasar kofin duniya da Super Eagles ta yi na 2022, an sallami Augustine Eguavoen daga mukaminsa kuma hukuncin zai fara aiki nan take.

“NFF ta janye kwantaragin da ta bai wa kafatanin tawagar kocin na shekara biyu, kuma nan take za su ajiye aikinsu,” a cewarsa.

Sanusi ya ce nan gaba kadan za a sanar da sabbin tawagar da za su jagorancin tawagar ’yan wasan Super Eagles don ta sake dawowa kan ganiya da kuma goyayya a harkar kwallon kafa.

“Mun gode wa daukacin tawagar kocin bisa gudunmawar da suka bai wa kasar nan, muna musu fatan alheri a rayuwarsu.”