✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Nijar ta wajabta wa ’yan Najeriya biyan harajin N700,000

Dokar za ta yi aiki ne a kan duk wani tasi da ke dauke da lambar Najeriya a kasar.

Gwamnatin Kasar Jamhuriyar Nijar ta haramta wa ’yan Najeriya masu sana’ar tukin tasi a kasar su sama da 200 ci gaba da aiki sai kowannensu ya biya ta harajin N700,000.

Sabuwar Dokar Sufuri ta wajabta w duk wani dan Najeriya da ya yi gudun hijira zuwa Nijar da ke son ci gaba da haya da motarsa mai dauke da lambar Najeriya, mallakar wata ’yar takarda kan kudin kasar 600,000 CFA, kwatankwacin N700,000.

Wadanda lamarin ya shafa da ke zama a Diffa a kasar, sun koka kan wanna batu, tare da rokon hukumomin Najeriya da na Nijar su shigo cikin lamarin don samun maslaha.

Malam Musa Abdullahi, dan asalin Karamar Hukumar Abadam a Jihar Borno ne, kuma shugaban ’yan Najeriya masu sana’ar tukin tasi a Diffa.

Ya ce, ’yan sanda da kwastam sun kwace musu motoci kusan 100 a mako guda saboda sabuwar dokar.

Ya kara da cewa, kudin da aka bukaci su biya din ya zarce kudin da yawancin motocin da suke haya da su don neman abin da za su ci da iyalansu.

Cikin wata muryarsa da aka nada aka yada, Shugaban Kungiya Masu Motoci a Diffa, Alhaji Gali Mustapha ya ce, dole wadanda lamarin ya shafa su gabatar da inshorar ECOWAS da sauran muhimman takardu kafin a sahale musu ci gaba da aiki a kasar.

Sai dai a nasu martanin, wasu mambobin kungiyar sun zargi shugaban kungiyar da haifar da rudani a Diffa.