✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Ofishin INEC ya kama da gobara

Ofishin ya kama da gobara a cikin dare kafin wayewar garin Juma’a.

Ofishin Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ya kama da gobara a tsakar dare kafin wayewar garin Juma’a.

Kakakin ’yan sandan Jihar Enugu, Daniel Ndukwe ya ce gobarar ta tashi ne a ofishin INEC da ke Obollo-Afor, a Karamar Hukumar Udenu ta Jihar ba.

“Bayan samun kiran neman dauki a babban ofishin ’yan sanda na Udenu, ada misalin karfe 9.40 na dare ranar 13/05/2021, cewa gobara ta tashi a ofishin INEC da ke Obollo-Afor.

“Jami’anmu da ke ofishin sun yi gaggawan isa wurin tare da sanar da hukumar kashe gobara halin da ake ciki domin a kashe wutar.

“Bayanan somin-tabi sun nuna matsalar wutar lantarki ce ta haddasa gobarar wadda ’yan kwana-kwana da ’yan sanda da mutanen gari suka yi nasarar kashewa kafin ta bazu zuwa sauran gine-ginen da ke harabar ofishin.

“Kwamishin ’Yan Sanda, Mohammed Aliyu, ya kuma sa a zurfafa bincike domin gano hakikanin abin da ya haddasa gobarar da kuma irin barnar da ta yi.”

Baya-bayan nan dai ana yawan kai hare-hare a kan gine-ginen gwamnati a yankin Kudu-maso-gabashin Najeriya.