✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Ramadan: Sarkin Saudiyya zai ba ’yan Najeriya 12,600 abinci

Iyalai Musulmi 2,300 a Najeirya ne za su amfana da kayan abinci a watan Ramadan

Gidauniyar Sarki Salman na kasar Saudiyya (KSrelief) za ta ciyar da ’yan Najeriya 12,600 ta hanyar raba wa iyalansu kanyan abinci a watan Ramadan da ke kara karatowa.

Gidauniyar ta bayyana cewa iyalai Musulmi 2,300 a Najeriya ne za su amfana da tallafin kayan abincin a watan Ramadan, domin su samu saukin rayuwa.

Ta bayyana haka ne a lokacin da take kulla yarjejeniya bayar da aikin ciyarwar da kungiyar jinkai ta Abibakr As-Sidiq Philanthropic Home (ASPH), wadda ta ba wa aikin rabon kayan abincin ga iyalan da za su amfana da tallafin.

Da suke sanya hannu a kan yarjejeniyar a Abuja, KSrelief da ASPH sun bayyana cewa manufar aikin ita ce ciyar da ’yan Najeriya Musulmi 12,600 da ke fama da matsanancin talauci.

Wadanda suka sanya hannu a yarjejeniyar ciyarawar su ne Wakilin KSrelief, AbdulKarim bin Abdulmohsen Al-Yousef tare da Mataimakin Shugaba Mai Kula da Ayyuka na Musammana a ASPH, Sultan Mohammed Saleh, wanda ya wakilci shugaban ASPH, Abdulrazzaq Ibrahim Salman.