✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Ranar Litinin jirgin kasan Abuja-Kaduna zai dawo aiki —Gwamnati

Kimanin wata takwas ke nan da dakatar da sufurin jirgin

Gwamnatin Tarayya ta sanar da Litinin mai zuwa a matsayin ranar da za a dawo da zirga-zirgar jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna.

Kakakin Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Kasa ta Najeriya (NRC), Yakub Mahmoud ne ya tabbatar da hakan ga wakilin Aminiya ranar Asabar.

Ya ce gabanin dawo da sufurin a ranar ta Litinin, hukumar za ta fitar da cikakkun bayanai ga jama’a ranar Lahadi.

Idan za a iya tunawa, a kwanakin baya ne Ministan Sufurin Jiragen Kasa na Najeriya, Mu’azu Jaji Sambo, ya sanar da cewa kafin karshen watan Nuwamban 2022 za a dawo da sufurin bayan shafe wata takwas da dakatar da shi.

Ministan dai ya ce za a dawo da sufurin ne kawai idan aka tabbatar da samar da isasshen tsaro a titunansa.

Ya ce dole a tabbatar da daukar wasu matakan tsaro kafin a kai ga dawo da sufurin, wanda ya hada da samar da na’urorin da za su rika sa’ido a kan kaiwa da komowar jirgin.

Sai dai wakilinmu bai iya tabbatar da ko kawo yanzu an kammala karkafa irin wadannan na’urorin a dukkan wuraren da ya kamata ba.

An dai dakatar da sufurin ne a watan Maris din da ya gabata, lokacin da ’yan ta’adda suka kai masa hari, inda suka kashe wasu fasinjojin suka kuma yi garkuwa da wasu.