✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Rikicin Ukraine: Romaniya za ta bai wa ’yan Najeriya gurabun karatu

An fara shirye-shiryen bai wa daliban damar ci gaba da karatunsu.

Gwamnatin Tarayya ta ce ta fara shirye-shirye da kasar Romaniya domin daukar daliban Najeriya da suka tsere wa rikicin kasar Ukraine, wadanda ke son ci gaba da karatunsu a jami’o’in kasar.

Wannan na dauke ne a cikin wata sanarwa da Ofishin Jakadancin Najeriya da ke Bucharest ya fitarcewa an bai wa daliban wa’adin wata guda domin yanke shawara.

Sanarwar ta ce, “Ofishin Jakadancin Najeriya da ke Bucharest a Romaniya, na farin cikin sanar da daliban Najeriya da ke ficewa daga Ukraine cewa an kammala shirye-shirye da wasu jami’o’i don ba su dakunan kwanan dalibai na tsawon wata guda.

“Duk wanda ya ke son cin wannan moriya ya tura sakon tes ga wadannan lambobi: +40 749 335 927, +40 786 091 964.”

Rikicin Ukraine ya sanya daliban Najeriya da dama da ke karatu a can hakura tare da dawowa gida Najeriya, don tsira da rayukansu.

Mako biyu ke nan da ake gwabza yaki tsakanin Ukraine da Rasha.