✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Ronaldo ya koma kungiyar Al Nassr ta Saudiyya

Wata majiya ta ce zai karbi albashi Fam miliyan 175 a shekara

Fitaccen dan wasan kasar Portugal, Cristiano Ronaldo ya rattaba hannu kan yarjejeniyar komawa buga wasa a kungiyar kwallon kafa ta Al Nassr da ke kasar Saudiyya.

Kafar labaran wasanni ta Sky sports ta ce dan wasan ya sanya hannu ne a kan yarjejeniyar shekara biyu a kungiyar da ke birnin Riyadh na kasar Saudiyya.

Wata majiya ta ce zai karbi albashin Fam miliyan 175 a shekara a yayin da kafar Marca ta ruwaito cewar yarjejeniyar ta shekara bakwai ce — zai yi wasa na shekara biyu da rabi sannan ya zama jakada.

Ana hasashen aikinsa a matsayin jakada ya kunshi taimaka wa Saudiyya karbar bakuncin Gasar Kofin Duniya na 2030 da hadin gwiwar kasashen Masar da Girka.

Kafar Al-Ekhbariya ta Saudiyya ta ce a watan Janairu Ronaldo zai fara murza leda a sabuwar kungiyar tasa.

Majiyoyin cikin gida a Al Nassr sun shaida wa kafar CBS cewa a ranar Juma’a da wasan ya rattaba hannu a kan yarjejeniyarsa da kungiyar.

Majiyar ta ce sai da dan wasan mai shekaru 37 ya yi gwajin lafiya na farko gabanin sanya hannu kan takardar yarjejeniyar, kuma a mako mai zuwa zai yi gwaji na biyu.

Dan wasan zai fara wasa a kungiyar Al Nassr ne wata biyu bayan sun yi baram-baram da kungiyarsa ta Manchester United da ke kasar Birtaniya.

Ana ganin komawar Cristiano Ronaldo Saudiyya da murza leda ya kawo karshen tashe sa a harkar tamola, amma kuma zai samu albashi mai tsoka.

Kawo yanzu dai Al Nassr da Ronaldo ba su yi tsokaci kan lamarin ba, ballantana su yi karin haske.

Amma a watan Nuwamba dan wasan ya ce ya ki amsa tayin Dala biliyan 305 daga wata kungiyar kwallon kafa a Saudiyya.

Tun bayan raba gari tsakanin Cristiano Ronaldo da Manchester United dai Al Nassr ta bayyana shirinta na daukar sa.