✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Ruwan sama ya rusa bene mai hawa biyu a Filato

Ana zargin babu wanda ya makale a baraguzon ginin.

Wani ginin bene mai hawa biyu ya fadi a garin Bukur da ke Karamar Hukumar Jos ta kudu, sakamakon wani ruwa da aka ka yi kamar da bakin kwarya.

Lamarin ya faru ne a ranar Lahadi da misalin karfe 8:30 na safe a cewar wani mazaunin garin wanda lamarin ya faru a idonsa.

Benen mai hawa biyu, wurin harkar kasuwanci ne a inda ginin ke dauke da kantin sayar da kayyakin bukatun yau da kullum, da kuma dakin ajiyar kayayyaki.

A lokacin da wakilinmu ya ziyarci wurin, ya taras da jami’an Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Kasa NEMA, da kuma Hukumar Kashe Gobara suna ta aikin wadanda suka makale a baraguzan ginin.

Sai dai mai benen da ya fadi, Mista Pam ya ce, a saninsa babu wani wanda ke cikin ginin, shi kadai ne a lokacin da ginin ya fadi.