✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Sakataren kungiyar Arewa ta ACF ya yi mutuwar fuju’a

Ya rasu bayan ya yanke jiki ya fadi a ranar Asabar, 4 ga Satumba, 2021.

Sakataren Gudanarwar Kungiyar Tuntuba ta Arewa (ACF), Alhaji Mohammed Sani Soba, ya kwanta dama.

Alhaji Mohammed Sani Soba ya rasu ne bayan ya yanke jiki ya fadi a ranar Asabar, 4 ga Satumba, 2021.

Sakataren Yada Labaran ACF, Emmanuel Yawe, ya tababtar a ranar Talata cewa, “Rasuwar ta kada mu matuka a ACF, inda ya shafe shekaru yana aiki har zuwa lokacin rasuwarsa.”

Ya bayyana mamacin da cewa mutumin kirki ne da ya hidimta wa kungiyar ta ACF a matsayin Sakataren Gudanarwa.

Mamacin tsohon Babban Sakatare ne a Gwamnatin Jihar Kaduna, bayan ya yi ritaya ya kama aiki da ACF a matsayin kwantaragi.

Sanarwar rasuwar da ACF ta fitar ta ce, “An haifi Soba ne a 1949 sannan ya yi karatu a cikin gida da kasashen waje a fannoni da dama na mulki da ayyukan majalisar dokoki.

“Ya taba zama Akawun Majalisar Dokokin Jihar Kaduna.”