’Yan Sanda shida ne suka rasu sakamakon zanga-zangar da ake gudanarwa saboda tsadar rayuwa a kasar Saliyo.
Gwamnatin kasar Saliyo to bayyana a ranar Alhamis cewa ’yan sanda biyun an kashe su ne a Freetown, babban birnin kasar, yayin da aka kashe uku a birnin Kamakwie, sai dayan da aka kashe Makeni.
Shugaban ’yan sandan, Insfekta William Fayia, ya ce akalla fararen hula biyu sun mutu bayan ’yan Sandan a birnin Freetown.
Gwannatin kasar dai a baya ta ce ana samun asarar rayuka sosai sakamakon zanga-zangar, sai dai ba ta fadi adadin ba.
Sai dai ta ce hakan na faruwa ne sakamakon daruruwan masu zanga-zangar da ke jefe-jefe da kone tayoyi.
Zanga-zangar kasar dai ta balle ne don nuna bacin ran ’yan kasar kan tabarbarewar tattalin arziki, da talauci da sauran matsaloli.
A ranar Laraba ne dai aka rufe hanyoyin sadarwar yanar gizo a kasar da kuma sanya dokar takaita zirga-zirga daga karfe 3:00 na rana don kashe kaifin zanga-zangar.