✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Mutum 50 sun mutu a hatsarin jirgin ruwa

Ana zargin jirgin na dauke da mutane 400 kafin aukuwar hatsarin.

Hukumomi a Dimokuradiyyar Congo sun tabbatar da mutuwar sama da mutum 50 sakamakon hatsarin jirgin ruwa da ya faru.

Kakakin Hukumar Kula da Tashar Jiragen Ruwan Kasar, Jose Misiso, ya ce mutane da dama sun bace.

Jirgin ruwan da aka makare shi da mutane fiye da kima, ya yi hatsarin ne bayan ya taso daga yankin Bumba zuwa Arewacin Mongala a ranar Laraba.

A cewar kakakin, an yi nasarar ceto mutum 30 tun bayan faruwar hatsarin.

Sai dai ya ce har yanzu ba a samu tabbacin adadin mutanen da suka bace ba.

Hukumomin kasar sun kuma bayyana cewa mutum 75 ne ake tunanin sun bace, yayin da kuma wanda suka kubuta suka shaida cewa jirgin ruwan na dauke da mutum 400 kafin ya yi hatsari.

Mutane da dama a kasar ta Congo sun koma amfani da jiragen ruwa a matsayin ababen sufuri, sakamakon, lalacewar da titunan kasar suka yi.

Sai dai a lokuta da dama ana samun mutane fiye da kima a jiragen ruwan da suke sufuri a kasar, wanda hakan na iya haddasa hatsari a lokuta da dama.