✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Sanata Hunkuyi ya fice daga jam’iyyar PDP

Jam'iyyar PDP na fata ficewar Sanata Hunkuyi daga cikinta zai kawo mata cigaba.

Sanata Suleiman Othman Hunkuyi ya fice daga jam’iyyar PDP reshen Jihar Kaduna.

Sanata Hunkuyi shi ne ya wakilci mazabar Kaduna ta Arewa a Majalisar Dattawa daga 2015 zuwa 2019 a jam’iyyar APC, ya sauya sheka ne bayan ya rasa kujerar takarar tasa.

Bayanin ficewar tashi na dauke ne cikin wata sanarwa da ya fitar cewa, “Ina sanar da ku ficewata daga jam’iyyar PDP. Don haka ina so shugabanni su shaida hakan.”

Mun yi kokarin jin ta bakin Sanata Hunkuyi, amma hakarmu ba ta cim-ma ruwa ba.

Amma Sakataren Jam’iyyar PDP a jihar, Ibrahim Wosono, ya tabbatar mana da ficewar Hunkuyi daga jam’iyyar, wanda ya ce suna fatan hakan zai kawo wa jam’iyyar cigaba.

“Tabbas, mun samu takardar ficewarsa daga mazabarsa, don haka muna masa fatan alheri tare da samun nasara ga jam’iyyarmu,” a cewarsa.

Ya ce Sanatan ya jima da daina shiga harkokin jam’iyyar, don haka a cewarsa ficewarsa ba za ta shafi jam’iyyar ba.

Hunkuyi ya yi takarar kujerar gwamnan Kaduna a karkashin inuwar jam’iyyar PDP a 2019, amma ya fadi a zaben fidda-gwani.