✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Sarki Sanusi ya jagoranci Sallar Idi a Kaduna

Sanusi ya dawo Najeriya daga Senegal, inda aka nada shi a matsayin Halifan Tijjaniyya kasar.

Tsohon Sarkin Kano kuma Halifan darikar Tijjaniyya a Najeriya, Muhammadu Sanusu II, ya jagoranci Musulmi Sallar Idi ranar Alhamis a Jihar Kaduna.

Jaridar Dateline da ake wallafa wa a shafin Intanet ta ruwaito cewa, an gudanar da sallar idin ne a filin da aka rushe Otel din Durba, sakamakon aikin gine da ake ci gaba da gudanarwa a Dandalin Murtala wanda aka saba bisa al’ada.

Sarki Sanusi ya isa Jihar Kaduna ce tun a ranar Talata daga Kasar Senegal, inda aka tabbatar da nadinsa a matsayin Halifan Tijjaniyya na Najeriya.

Rahotanni sun bayyana cewa, tsohon Sarkin Kanon ya dauki al’adar kai ziyara tare da shafe tsawon lokacin a Jihar Kaduna tun bayan sauke shi da Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya yi fiye da shekara daya da ta gabata.

Aminiya ta ruwaito cewa, a yau Alhamis ce daukacin al’ummar Musulmi suka yi bikin Idin Karamar Sallah ta bana, bayan ajiye azumin watan Ramadana da suka yi a ranar Laraba.