✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Sarkin Daura ya sake auro budurwa mai shekara 22

An yi auren ba tare da wasu manyan shagurlgula ba, kuma bar amarya ta tare

Mai Martaba Sarkin Daura, Alhaji Faruk Umar Faruk, ya sake angwancewa da budurwa mai kimanin shekaru 22 mai suna A’isha Yahuza Gona.

Aminiya ta samu rahoto cewa auren an daura shi a garin Safana da ke Jihar Katsina.

Majiyarmu da ta nemi a sakaya sunanta daga garin na Safana inda aka dauro auren ta ce, da fara neman auren da yin komai an yi shi ne cikin sati guda.

Kazalika, an yi auren ne tamkar a asirce domin babu wani shagalin bikin da aka yi.

Ita dai A’isha, amaryar Sarki, ’ya ce ga Alhaji Yahuza Gona, tsohon Shugaban Karamar Hukumar Safana a lokacin da aka taba yin zaben kananan hukumomi ba tare da jam’iyya ba.

Tuni dai amarya na dakin mijinta kamar yadda wata majiyar ta shaida mana.