✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Sarkin Zazzau ya umarci limamai su gudanar da addu’o’in samun tsaro

Hare-haren baya-bayan a yankin Masarautar Zazzau sun sa sarkin ya dakatar da wasu tafiye-tafiyensa.

Sarkin Zazzau, Ahmad Nuhu Bamalli, ya bukaci limaman addinai da ke masarautarsa su fara gudanar da addu’o’i na musamman domin samun tsaro da zaman lafiya a yankin da ma Najeriya baki daya.

Sarkin Zazzau, ta wata sanarwa da ya fitar ta bakin jami’in yada labaransa, Abdullahi Aliyu, ya ce gudanar da addu’o’in ya zama wajibi, ganin yadda ’yan bindiga ke ci gaba da yi wa mutanen masarautar kisan gilla.

Ya yi kira ga Musulmi da su yi amfani da kiran nasa wajen gudanar da addu’o’i a lokacin salloli biyar na farilla, Kiristoci kuma a lokacin ibadarsu.

Da yake jajantawa ga iyalan wadanda aka kashe a harin, Sarkin Zazzau, ya kuma yi addu’ar samun sauki ga wadanda suka samu raunuka a hare-haren.

Hare-haren baya-bayan a yankin Masarautar Zazzau sun sa sarkin ya dakatar da wasu tafiye-tafiyensa.