✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Senegal ta bukaci Jamus ta bar dakarunta a Mali

Shugaban na Senegal ya bukaci a ci gaba da bai wa Mali kariya.

Shugaban Kasar Senegal, Macky Sall, ya roki Jamus da ta ci gaba da girke dakarun sojinta a Mali, saboda rashin tabbas da ya mamaye kasar sakamakon janyewar dakarun Faransa.

Bayan gana wa da shugaban Jamus Frank-Walter Steinmeier a Dakar, Sall ya ce bai dace kowa ya gudu ya bar Mali ba, saboda haka yana da kyau dakarun Jamus su ci gaba da zama a kasar.

Kasar Jamus na da sojoji 1,170 da ke aiki a karkashin dakarun samar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya a kasar Mali.

A makon da ya gabata ne Faransa ta sanar da shirin janye dakarunta da su ka shafe shekara tara suna yaki da ta’addanci a yankin Sahel daga Mali, biyo bayan sabanin da suka samu da hukumomin kasar a karkashin gwamnatin mulkin soji.

Hakan ya sa ministar tsaron Jamus, Christine Lambrecht, ta bayyana shakku a kan ci gaba da barin dakarun kasar a Mali bayan janyewar Faransa.

Lamarin da ya fara jefa shakku da tsoro a kasashen da ke makwabtaka da kasar Mali.