✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Sojojin Rasha na shirin ficewa daga Kazakhstan

Dakarun za su dakatar da aikinsu na samar da zaman lafiya a kasar Kazakhstan da ta fada cikin rikici.

Dakarun Sojin Kasar Rasha sun fara ficewa daga Kazakhstan a ranar Alhamis bayan da Shugaba Vladimir Putin ya bayyana cewa aikinsu na kwantar da tarzomar da ta biyo bayan zanga-zangar kasar ya juye zuwa rikici ya kammala.

Putin, a cikin jawabinsa, ya ce aikin dakarun kungiyar tsaro ta CSTO ya kawo karshe a Kazakhstan bayan da aikinsu ya janyo ce-ce-kuce daga kasashen duniya ciki har da Amurka.

Rundunar tsaron CSTO da ke matsayi iri daya da na NATO na kunshe da dakarun kasashe shida — Rasha, Belarus, Armenia da kuma Tajikistan baya ga Kyrgystan da Kazakhstan — wadanda suke aiki tare don dakile barazanar tsaro a tsakaninsu.

Sai dai aikinsu a wannan karon ya gamu da kakkausar suka musamman bayan tsoma bakin Amurka da ake ganin shi ya sake tunzura masu zanga-zangar ta Kazakhstan, dalilin da ya tilasta dakatar da aikin da ya zama irinsa na farko a tarihi.

A ganawar Shugaban Kungiyar CSTO kuma Ministan Rsaron Rasha, Sergei Shoigu da Shugaba Vladimir Putin, ya tabbatar da cewa dakarun za su fara ficewa daga Kazakhstan a ranar Laraba mai zuwam su kuma kammala a ranar 22 ga watan nan da muke ciki.

Tun da farko Shugaba Kassym-Jomart Tokayev ya bukaci shigar Rasha kasar don kwantar da rikicin, sai dai isar dakarun ya sauya salon rikicin.

’Yan kasar ta Kazakhstan sun fara zanga-zangar ce bayan gwamnatin kasar ta yi karin farashim man fetur, baya ga tsadar kayan masarufi da suka yi tashin gwauron zabo.