Fitaccen jarumin fina-finan Hausa na Kannywood kuma mawaki, Adam A. Zango, ya dauki nauyin karatun dalibai 101, a makarantar Professor Ango Abdullahi International School, Zariya jihar Kaduna.
Shugaban kamfanin Prince Zango Production Nigeria Limited, ya ce fitaccen jarumin ya biya kudi Naira Miliyan 46.75 na wa’adin shekara uku akan karatun daliban da ya dauki nauyi.
“Babban burina shi ne taimakon marayu da talakawa musamman kananan yara.” In ji Adam Zango.