Gwamnan jihar Kebbi Atiku Bagudu ya amince da biyan Naira miliyan 400 don daliban jihar da zasu shiga manyan makarantun da ke yankunan kasar a zangon karatu na 2017/2018.
Sakataren watsa labarai na Gwamnan Alhaji Abubakar Dakingari, ne ya bayyana hakan yau Alhamis a Birnin Kebbi.
Dakin gari ya ce, an kammala kididdige adadin kudaden da za a biya manyan makarantu sakandare da sauran jami’o’in kasar.