✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Jarrabawar ji a jika

A fadin Ifirikiyya Jahilci ya zam abin kiyayya Ilmu muke nuna wa soyayya Masana ai ta gogayya Ko mun bar adawa da hamayya Koyi ka…

A fadin Ifirikiyya

Jahilci ya zam abin kiyayya

Ilmu muke nuna wa soyayya

Masana ai ta gogayya

Ko mun bar adawa da hamayya

Koyi ka koyar babu jayayya

’Yan makaranta ai ladabi da biyayya

Dodon Dodoridon duniya

Dawurwuri da duminiya

Malamai na ta hatsaniya

Tura ta kai bango

Wasu sun yi nadin damben shago

Ba sa dubin wulwulawar agogo

Uhm tsallen badaken Gizago

Dafdalar cikin kango

Duk wani mai gyara

Sai ya jure wa terere

Har da masu suka da sare-sare

Ko karo da kan kure

Bayan kuka sai an dara

Ai ta kokarin kauce wa asara

Babu tsimi ba dabara

Mai-duka yai mana sutura

Mu daina yi wa juna hantara

Domin tana sanya wasu kangara

’Yar gagara

An ce ta iya fitsara

Al’umma ta sanya mata kangara

A taimaka mata hankali ya tattara

Wahala ce tai mata makara

Kar a kira wane dan iska

Shi ma sai yai maka cin fuska

In an buga mai rauni zai sha faska

Miyagu sun washe kudin taska

Har wani yai tutiyar babban gwaska

Fitintinu sun zame mana kaska

Juhala ta saka mu tsaka

Adala muke fafutika

Jarrabawar ji a jika

Faduwar daraja ko makin daukaka

kolon malam na walgigi

’Yan dugwi-dugwi an shiga kangi

Iyaye na ta kugi

Hukuma na hargagi

Marasa kan gado na ta magagi

Can a Jihar bayan Kada

Na ga mai na-kada

Na borin kama kada

Direbobin alli a kan gada

An wancakalar da masu gada-gada

Jarrabawa ce an gwada

An gaza cin makin gina gida

An zo ana ta fada

An haifar da rudanin kida

Babu kyakkyawar ta’ada

A kwadago muna neman lada

A karo mana da la’ada

Ilmin ’ya’yanmu ya fadada

Malumma a daina kurda-kurda

Sai mu samu abin cin ragadada

Ban da tada kan adda

Ko yawan kassada

kazanta ke jawo kuda

Mu himmatu kowa ya sududa

kasarmu ta samu sa’ida

Direbobin alli

A yi aiki da hankali

Ban da kwasar albashi ai shagali

Godiyar sakarci na sukuwar dandali

Wagagen littafi da Watsattsaken fasali

Yaya za horar da Bokan Turai

Idan dan biro ya zam sakarai

’Yan dugwi-dugwi sun ga bambarakwai

Akalar aji ta zam rai-mutu kwakwai

An fasko jirginsu sarai-sarai

Gwamna el-Rusau

Abokin Malam Rubdigau

Bulalarka ba ai mata sagau

Darandakau Jikan Kwasau

Ka zama makasau

Tsaurara tsarin tsaro

Tsinin tsintsiya ya shashsharo

Kwaramniyar kwararo-kwararo

kazantar juhala an tattaro

Masu tabbatar da adala a hallaro

Saranka ya zam dubin bakin gatari

Kar a bari korarru su zam batagari

A ba su abin zaman gari

Kada al’umma ta fada garari

Mahukunta a cire mana sasari

Gwamna gwarangwam na jihar Bayan Kada ya shiga bakin duniya saboda jarrabawar ji a jika da ya aiwatar har ta jikkata direbobin alli a daukacin fadin jihar. Wannan lamari ya haifar da ce-ce-ku-ce a kasar nan dungurungum, har ta kai ga Dodorido ya ja bakinsa ya yi gum. Aminiyawan aminan Amintacciyar jaridar kasar Haurobiya suna ta guna-guni, wai Gwamna el-Rusau abokin Malam Rubdigau ya yi wa Direbobin alli bulalar da ba a yi mata sagau. Ni kuwa na ce DARANDAkAU jikan KWASAU ka zama MAkASAU.

Batu na ingarman karfen karafan titin tarragon kwangiri, matukar Gwamnan Bayan-Kada yana sara da dubin bakin gatari, ba na tsammanin zai bar korarru, domin yana da zabi ko dai ya maishe su HORARRU ta yadda za su zama kWARARRU wajen nusar da ’yan dugwi-dugwi dimbin DABARRU don kwarewa a fannin watsattsake da buda wagagen litatttafai, ta yadda za su ji dadin baje mana ilimi a faifai; masu yada JUHALA kuwa in ba a yi sannu ba, sai an hango su da dan kamfai. 

’Yan makarantar Dodorido masu koyon watsattsake da buda wagagen littattafai a wannan farfajiya, matukar mun yarda da cewa fannonin ilimi a kasar nan na fama da jinya har ta kai ga an dade ana laluben minjirya da rawaya da za su zaburar da kuzarin al’ummar da ke fama da ciwon shawara, har su ci awara kowa ya samu warwara.

Tunda Baban-burin-huriyya ya mara wa Gwmana el-Rusau baya, kuma muna da masaniyar cewa Baba tambarin yaki da tsilli-tsillin matsalolin al’umma ne, kuma baya mai goya marayu, shi ya sa nima na bi, amma ba na son kinbibi a tsakanin masu tunkudo rawunna da kallabi; ko kiren karairayi a rambada musu zabibi, su sauya launi, har mu ci gaba da zama cikin rauni. Hattara dai al’umma. Kowa ya kara himma, a daina hauma-hauma. Watakiula wannan ne dalilin da ya nusar da Gwamna gwarangwam na Jihar Kududdufi ke yunkurin yi wa direbobin allin jiharsa JARRABAWAR JI A JIKA, don su ji dadin kamun kifi, ’ya’yanmu su ji dadin yankawa da tsitaka mai kaifi. Da sun dunsume kururrunsu, sai su ji dadin falle mujalllu da jaridu da wagagen litattafai shafi-shafi.

Lallai hakki ne da ya rataya akan kowane dan kasa nagari ya tabbatar da cewa mahukuntan Bayan-kada sun kwance mana sasari, don gudun kada a jefa al’umma cikin garari. 

Gwamna gwarangwam in ka ciza, ka hura. A debi wani ba’ari na sukurkutattun direbobin alli a mayar da su zakakurai koda ba a fannin tukin alli ba, ta yadda za su zamto nagargaru, don kada su karke da zama kangararrrun kadangaru masu bula mana garu. Sauran masu hankali a kwanyarsu ku bijiro da duk wasu shawarwari da za su sanya mu kai ga gaci, don daukar tsintsiya mu share duk wata kazanta da ke yada cuta a farfajiyar koyon watsattsake da buda wagagen littafai, don kada juhala ta yi mana tsirara mu rika tutiya da kamfai, alhali kwanyar kwakwalen mafi yawanmu ta zama kufai.