Kamfanin jirgin saman Air Peace ya dawo bakin aiki a Kaduna bayan da kamfanin ya dakatar da harkokinsa a jihar bayan kafa dokar hana fita ta sa’o’i 24 sakamakon rikicin jihar.
Air Peace ya dakatar sufurinsa daga Legas zuwa Kaduna ko Kaduna zuwa Legas a ranar 21 ga Oktoba 2018, sun yanke shawarar ne da nufin tabbatar da tsaro rayuwar ma’aikatan kamfanin da abokan hulda.