✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Kotu ta ba Emefiele izinin fita daga Abuja

Kotu ta sahale wa tsohonn Gwamnan CBN, Godwin Emefiele, fita daga yankin Babban Birrnin Tarayya.

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta ba wa tsohonn Gwamnan Baban Bankin Najeriya (CBN) Godwin Emefiele, izinin fita daga yankin Babban Birrnin Tarayya.

A ranar Alhamis kotun da ba da izinin bayan bukatar hakan da lauyan Emefiele, Mathew Bukka, SAN ya gabatar, yana neman ta sauya sharuddan belinsa da ta bayar.

A ranar 23 ga Nuwamba, 2023, Mai Shari’a Hamza Mu’azu ya ba da belin Emefiele, wanda Hukumar yaki da masu karya tattalin arzikin kasa (EFCC) ta gurfanar kan zargin badakalar biliyoyin kudade a lokacin shugabancinsa a CBN.

A lokacin, Mai Shari’a Hamza Mu’azu ya shardanta wa Emefiele ajiye kudi Naira miliyan 300 da kuma kawo mutum biyu wadanda kowannensu ya mallaki gida a unguwar Maitama a Abuja su tsaya masa.

Haka kuma alkalin ya shardanta wa tsohon gwamnan na CBN cewa ba zai fita daga Abuja zuwa wani waje ba.

Amma a zaman ranar Alhamis, lauyansa, Matthew Bukkak, ya bakaci a janye sharadrin hana shi fita daga Abuja, yana mai cewa a matsayin Emefiele na babban mutum, ba zai tsere ba idan aka yi masa sassaucin fita daga Abuja.

Lauyan ya kara da cewa hasali ma takardunsa na tafiye-tafiye suna hannun koutu don haka babu halin ya tsere.

Lauyan hukumar EFCC Rotimi Oyedepo, SAN, bai kalubanci bakutar lauyan na Emefiele ba, amma ya ce, “Duk da cewa takardun nasa suna hannun kotu, amma ya kamata ya rubuta alkawarin cewa ba zai bar Najeriya ba har sai an kammala shari’arsa.

“Wannan ba yana nufin cewa ina zargin sai iya tserewa,” in ji Oyedepo, wanda ya ce, “an sha samun wadanda takardunsu na tafiye-tafiye ke hannun kotun sun tsere daga Najeriya, inda suke zuwa su ba da takardar rantsuwar karya cewa takardun nasu sun bace.”

Bayan sauraron bangarorin, alkalin ya sahale wa Emefiele fita daga Abuja, bisa sharadin ya kasance a cikin Najeriya har sai an kammala shari’ar.

“Kotu ta amince da bukatar wanda ake zargi. Amma wajibi ne ya kasance a Najeriya har sai ab kammala shari’arsa,” in ji alkalin.