✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Masu laifi 93 sun shiga hannun ’yan sanda a Kano

Ana zargin wadanda da aka kama da shirin kawo cikas ga rantsar da sabon gwamnan Jihar.

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, ta kama mutum 93 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban cikin mako guda a jihar.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Kano, Muhammed Usaini Gumel ne ya bayyana haka yayin da yake zantawa da manema labarai a ranar Laraba.

Gumel ya bayyana cewa binciken farko da suka gudanar ya tabbatar da cewa wadanda ake zargin na da hannu wajen daukar nauyin kawo cikas a bikin rantsar da sabon gwamna da mataimakinsa a Jihar.

Ya ce an samu wasu daga cikinsu dauke da muggan makamai, “da miyagun kwayoyi da kuma shirye-shiryen amfani da makaman domin yin fashi da kuma kawo cikas ga bikin rantsar da sabon gwamna.

“Don haka duk wadanda ake zargin za a gurfanar da su a gaban kotu kan wadannan laifuka.

“Ina da yakinin cewa kotunan shari’a za su dauki matakan da suka dace.”