A yau Laraba karamin ministan muhalli Alhaji Ibrahim Jibrin ya mika takardarsa ta yin murabus ga shugaban Najeriya Muhammadu Buhari yayin taron majalisar ministoci na mako-mako.
Ministan ya ajiye aiki ne bayan da aka zabe shi a matsayin wanda za a nada ga mukamin sabon sarkin Nassarawa dake jihar Nasarawa.
An nada ministan ne a watan Disamba ta 2015 bayan tantancewar majalisar zartarwa.