✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

NEMA ta bayyana jihohi 14 da za su iya fuskantar mummunar ambaliya a makon nan

NEMA ta ce za a yi ambaliyar ne daga 4 zuwa 8 ga watan Yuli

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Kasa (NEMA) ta bayyana wasu jihohi 14 da ta ce akwai yuwuwar a sami mummunar ambaliyar ruwa a cikinsu nan ba da jimawa ba.

A cewar hukumar, ana fuskantar barazanar samun ambaliyar ce daga tsakanin 4 zuwa 8 ga watan Yulin 2023 a yankuna 31 da ke cikin jihohin.

Gargadin dai na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Ko’odinetanta na shiyyar Legas, Ibrahim Farinloye, ya fitar ranar Laraba.

A kan haka ya yi kira ga dukkan masu ruwa da tsaki a jihohin da lamarin ya shafa da su dauki matakan da suka dace domin kiyaye rayuka dukiyoyin jama’a.

Hukumar ta ce yankunan sun hada da:

Filato: Langtang, Shendam

Kano: Sumaila, Tudun wada

Sakkwato: Shagari, Goronyo, Silame

Delta: Okwe

Kaduna: Kachia

Akwa Ibom: Upenekang

Adamawa: Mubi, Demsa, Song, Mayo-belwa, Jimeta, Yola

Katsina: Katsina, Jibia, Kaita, Bindawa

Kebbi: Wara, Yelwa, Gwandu

Zamfara: Shinkafi, Gummi

Borno: Briyel

Jigawa: Gwaram

Kwara: Jebba

Niger: Mashegu, Kontagora

Ibrahim Farinloye ya kuma yaba wa Sashen Gargadi Kan Ambaliya (FEWS) na hukumar na Ma’aikatar Muhalli ta Kasa da ke Abuja saboda fitar da bayanin a kan lokaci. (NAN)