✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Uwar gidan Shugaban kasa: Ba haka ake siyasa ba

Edita ina so ka ba ni dama sharhi kan maganganun matar shugaban kasa da take ba da umurni, a yawon yakin neman zabe “campaign” duk…

Edita ina so ka ba ni dama sharhi kan maganganun matar shugaban kasa da take ba da umurni, a yawon yakin neman zabe “campaign” duk wanda ya zo musu da campaign cewa canji, to su jefe su, gaskiya wannan bai dace ba; ba haka ake siyasa ba sam-sam. Kuma su ma ’ya’yan jam’iyyun nan guda biyu, wato PDP da APC, su gaya wa magoya bayan su cewa, tada fitina a kasa ba shi ba ne zai kawo cin zabe, tunda har shugabannin sun sa hannun a kan yarjejeniya gudun tashin hankali mai zai hana mu bari, har akai ga lokacin zabe 28/4/2015 in sha Allahu a gani, wanda ya iya karatunsa, sai ya wanke allonsa, wanda ya ci zabe a ba shi da fatan za mu guji tada zaune tsaye a wannan lokacin. Ubangiji Allah ya sa a yi zabe lafiya amin. Daga Ilyas Idris Fahad Suleja.

Zan kwato hakkin talaka
Yanzu mu dai a Najeriya talaka ya zama tamkar shara, an manta da talakawa, an manta da rayuwar talakawa sai zabe ya zo, a zo a yi ta yi musu karairayi, wadanda ya kamata duk wani mai hankali a ce ya gane. Talaka yanzu ya zama aikin gwamnatin ma da yake yi ba biyansa hakkinsa ake yi ba. Ni ba dan albashi ba ne,ni dan makarantane, amma na sha alwashin Insha Allahu da ikon Allah sai na kwato wa ’yan uwana talakawa ’yancinsu. Ai da rarrafe akan tashi. Ina fatan ’yan uwana talakawa idan sun ga sakona za su tayani da addu’a, domin in kai dukkan matsayin da zan kwato mana ’yancinmu. Daga Usman dangundumar Jama’are 08163055770.

Mun gano karyar PDP
Assalam Aminiya. PDP da gwamnatin Jonathan ku sani karairayinku sai dada bayyana suke yi a fili. Kun fito kuna cewa an kwantar da Janar Buhari a asibiti a birnin Landan, sai ga shi ta bayyana karara Buhari ya gabatar da jawabi a dakin taro na Chatham House cikin koshin lafiya, kuka sake daukar mutane haya wai su je suna daga kwali wai da sunan zanga-zanga. To, ku sani Buhari ya zama gamji sara da sassakar PDP ba zai hana shi tofo ba. Ta Allah ba taku PDP. Daga Kabiru Myball 08139498956. 0802 447 3144

Kira ga Goodluck
Edita. Don Allah Ka taimake ni sakon nan ya isa kunnen Shugaban kasata Najeria, Dokta Good Luck Ebele Jonathan. Mu fa bukatarmu, ita ce a kare mana rayuka da dukiyoyin, ba a tara ma’aiikatan gwamnati ana ’yan guje-guje ba. Domin alama ce ta nuna nishadi a daidai lokacin da asarar rayuka yake karuwa a Arewacin Najeriya. Daga Isma”il Alkyabba Funtuwa.

Jonathan zai samu kuri’a a Kano
Assalamu alaikum al’ummar Najeriya sakamakon rubuto sako da na yi akan cewa a zabi cancanta, wasu ’yan ba ni na iya, ’yan kanzagi suka yi min tes, wasu suka bugo mini waya, suka ce ban yi daidai ba, a bisa haka na janye kalamaina, a zabi Dokta Goodluck Ebele Jonathan Mai Nasara. Ku sani cewa, Allah ne mai kashewa da rayawa a Najeriya, babu jam’iyyar da babu kafiri, ku sani yada jita-jita da farfaganda, ba shi ne zai yi mana maganin abin da ke faruwa a kasar nan. A wannan karon mu Kanawa sai mun bai wa kowa mamaki, Jonathan zai samu kuri’u masu yawa a Kano, Malam Salihu Sagir Takai ya zama gwamna in sha Allah. Daga Abdulrashid Loi dandago Kano 08116514183.

Kira ga Aminiya
Edita Aminiya, da fatan alkhairi nake sanar da kai yadda jaridar Aminiya ba ta shige ni. Haka labaran Muryar Amurka bOA Hausa. Jaridar Aminiya ta 24/10/2014 shafi na 25, na ga hoton Kabiru Fagge da abokan aikinsa na bOA Hausa. Ina rokon Edita don Allah ya zakulo mana sunayensu. (DS Narogo) 08034507166.

Ga ma’aikatan Aminiya
Ma’aikatan jaridar Aminiya ina yi muku fatan alkhairi, Allah ya kare ku daga sharrin makiya. Amin. Daga kanwar Maikawo 08034843475.

Godiya ga Aminiya
Ga labarai masu kayatarwa, musamman ma ga kannywood. Aminiya muna nan muna sauraron ku, mu ji ya Ali Nuhu da Zango suka karasa. Daga Abbakar Barkindo Maiduguri.

Jinjina ga Gwamna Shema
Salam. Edita da fatan kana lafiya amin. Don Allah ka ba ni dama in yi jinjina da yabo ga Gwamna Shema na Jihar Katsina. Hakika Gwamna Shema ka yi rawar gani a Jihar Katsina, mu dai Katsinawa sai dai godiya. Gaba dai, gaba dai Shema. Allah ya ja zamanin ka, Sarkin Fulanin Katsina. Daga Hon. Shamsu Muhammed Katsina, 07039878892.

Ta’aziyyar Sheikh Al-Adamawi
Salam Aminiya ku mika min sakon ta’aziyyata ga iyalai da jama’ar Jihar Kaduna, na rasuwar babban malaminmu, Shaikh Muhammad Bello Al-Adamawi. Allah ya rahamshe shi amin. Daga Maman Safwan Kaduna.

Ta’aziyyar Sheikh Al-Adamawi
Salam. Editan Aminiya! Don Allah ku ba ni dama na mika wa al’ummar Musulmin Najeriya, musamman na Jihar Kaduna ta’aziyar rasuwar Sheikh Muhammad Bello Ahmad Al-Adamawy. Allah ya jikansa da rahama. Mu ma idan tamu ta zo Allah ya sa mu cika da kyau da Imani. Daga Mudassir Ibrahim Mando, Jihar Kaduna (Sakataren kungiyar Muryar Talaka na kasa, Reshen Jihar Kaduna) 08024122559.

Kira ga matasa
Ina kira ga ’yan uwana matasa, ku natsu, ku watsar da harkar shaye-shaye don ba shi da amfanin komai a gare ku. Mu tuna fa wata rana mu ne manyan gobe, masu fada aji; in mutum ya haukace wa zai saurare shi? Don haka mu yi hattara. Daga Isah Dilwaala Abuja 0703 637 9291.

Ina alfahari da Mediatrust
Hakika ina alfahari da jaridun kamfanin Media trust, yau na cika shekaru 10 da fara karanta jaridunku, Allah ya kara daukaka amin. Daga Mustapha dalhat Gaya (NSCDC).

Hattara ’yan 419
Salam. Edita ka sanar da masu karanta Aminiya, ni dai na gamu da ’yan 419, domin sun kirani, wanda ya kirani ya ce na yi sadaka da Alkur’ani, wanda ba a yi amfani da shi ba; inna yi hakan, sai na gaya musu lokacin da zan kira shi, sai na ce gobe in Allah ya yarda zan kira. Ban kira shi ba goben, bayan kwana daya, sai wannan lambar ta turo min da sakon na cire Naira dubu 750, kuma ka turo da wata lamba mai dauke da sunan Femi, wai in kira shi. Hattara dai ’yan uwa. Daga Yakubu Abdullahi Fulatan 08065192933.