✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

2023: Yadda APC za ta tantance Tinubu

Majiya ta kusa da dan takarar ta ce tuni kwamitin ya tuntubi Tinubu dangane da batun tantancewar.

A ranar Litinin din nan ake sa ran Jagoran Jam’iyyar APC kuma dan takarar Shugaban Kasa a jam’iyyar, Asiwaju Bola Ahmed, zai bayyana gaban kwamitin tantancewa ’yan takara don a tantance shi.

Majiya ta kusa da dan takarar ta ce tuni kwamitin ya tuntubi Tinubu dangane da batun tantancewar.

A cewar majiyar, “Karfe 4 na rana kwamitin ya tsayar don tantance Tinubu.”

Bayanan da APC ta fitar sun nuna baki daya, ’yan takarar shugaban kasa 23 ne kwamitin zai tantance, inda za a soma tantace 11 a ranar Litinin, ragowar 12 kuma zuwa ranar Talata.

Ga jerin sunayen ’yan takara da ake sa ran kwamitin zai tantance kamar haka:

  1. Chukwuemeja Uwaezuoke Nwajiuba
  2. Badaru Abubakar
  3. Robert A. Boroffice
  4. Uju Ken-Ohanenye
  5. Nicholas Felix
  6. Nweze David Umahi
  7. Ken Nnamani
  8. Gbolahan B. Bakare
  9. Ibikunle Amosun
  10. Ahmed B. Tinubu
  11. Ahmad Rufai Sani
  12. Chibuike Rotimi Amaechi
  13. Oladimeji Sabon Bankole
  14. John Kayode Fayemi
  15. Godswill Obot Akpabio
  16. Yemi Osinbajo
  17. Rochas Anayo Okorocha
  18. Yahaya Bello
  19. Tein Jack-Rich
  20. Christopher Onu
  21. Ahmad Lawan
  22. Ben Ayade
  23. Ikeobasi Mokelu

Jam’iyyar ta tsayar da ranakun 6 zuwa 8 ga watan Yuni a matsayin lokacin da za ta gudanar da zaben fid-da-gwani a tsakanin ’yan takarar nata don tsayar da wanda zai yi mata takarar shugaban kasa a zaben 2023.