✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Tsawa ta kashe ’yan uwa 2 da dabobbi 144 a Sakkwato

Ruwan sama da tsawar sun yi sanadin rushewar gidaje da dama.

Wasu kananan yara ’yan uwan juna sun gamu da ajalinsu yayin da tsawa ta fada musu a kauyen Ja’oje a Karamar Hukumar Wamakko ta Jihar Sakkwato.

Kananan yaran masu shekara tara da kuma 11 masu suna Hamida da Maryam sun gamu da ajalin nasu ne a lokacin da suke barci a yayin da tsawar ta kayar da dakin da suke ciki.

  1. ‘Dangote da BUA ke da izinin kawo sukari daga waje’
  2. AC Milan ta dauki Oliver Giroud daga Chelsea

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Daraktan Hukumar Agajin Gaggawa ta jihar, Mustapha Umar, ya ce dabobbi 144 sun mutu a sanadiyyar tsawar.

Ya ce tsawar ta fado ne a sakamakon mamakon ruwan sama da aka tafka a ranar Alhamis ta kuma rusa gidajen mutum sama da 177.

A cewar jami’in, hukumar da wasu kungiyoyi masu zaman kansu a jihar sun ziyarci kauyen don gudanar da bincike kan irin barnar da tsawar ta yi.

Ya tabbatar da cewa mutum biyu ne suka rasa rayukansu a iftila’in, amma ana ci gaba da bincike don gano ko akwai karin wasu da abun ya shafa.