✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An kama tsohon Shugaban Karamar Hukumar ‘mai taimakon’ ’yan bindiga

Ana zargin da daukar nauyin ’yan bindiga da kuma alaka da sace daliban Kankara

Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Katsina a kama wani tsohon Shugaban Karamar Hukumar Jibiya bisa zargin taimaka wa ’yan bindiga a Jihar.

An dai cafke Haruna Musa Mota ne bisa zargin taimaka wa da kuma daukar nauyin ’yan bindiga da masu garkuwar da suka addabi sassan Jihar.

A wani sakon murya da ya karade kafafen sa da zumunta na zamani a karshen makon da ya gabata, an zargi Haruna Mota da tattaunawa da daya daga cikin wadanda suka sace daliban makarantar Sakandiren Kankara a kwanakin baya.

Da yake tabbatar da kamen ranar Litinin, Kakakin Rundunar, SP Gambo Isah ya ce tuni aka gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu, kuma yanzu haka yana nan a tsare a gidan yari.

“Gaskiya ne mun gurfanar da shi kuma zarge-zargen da ake masa sun hada da hadin baki, taimaka wa ’yan bindiga, ’yan fashi, masu garkuwa da kuma ta’addanci,” inji kakakin.

A baya dai Gwamnatin Jihar Katsina ta sha zargin cewar ana yi wa yakin da yake yi da bata-garin zagon kasa ta hanyar tallafa musu da bayanai da kuma kudade.