✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

UEFA ta dauke wasan karshe na ‘Champions League’ daga Rasha

Matakin ya biyo bayan kaddamar da hare-hare da Rasha ta yi a kam Ukraine.

Hukumar Kwallon Kafa ta Turai (UEFA) ta dauke wasan karshe na Gasar Cin Kofin Zakarun Turai wanda za a buga a birnin St Petersburg na kasar Rasha zuwa birnin Paris na kasar Faransa.

Matakin ya biyo bayan kaddamar da hare-hare da kasar Rasha ta yi ne a kan Ukraine ranar Alhamis.

Tun ranar ta Alhamis hukumar ta kira taron gaggawa, inda ta shiga tattaunawa a kan yiwuwar dauke wasan karshen daga Rasha.

Tun kafin fara gasar ta bana, UEFA ta fitar da birnin St Petersburg a matsayin wurin da za a buga wasan karshe.

Tuni aka fara nuna kin jinin fara yakin da Rasha ta kaddamar a kan Ukraine a wasannin gasar Europa da aka gudanar ranar Alhamis.