✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Boko Haram: An kwana ba a rintsa ba a Geidam

Mazauna garin sun kwana cikin zullumin yiwuwar hari daga kungiyar ISWAP

Jama’a sun yi ta guje-guje a cikin dare, suka kuma kwana cikin zullumi a garin Geidam na Jihar Yobe, bayan jin fashewar wasu abubuwa masu karfin gaske.

Jin wannan kara mai karfi ya haifar da fargabar yiwuwar kai hari daga mayakan kungiyar Boko Haram/ISWAP a tsakanin mazauna gari, wanda shi ne hedikwatar Karamar Hukumar Geidam.

Wani mazaunin garin da ya bukaci Aminiya ta sakaya sunansa ya bayyana cewa “Mun ji wasu kararraki da suka sa muka garzaya gida muka kulle kofofinmu, muna zaune cikin firgici kuma ba mu san ainihin abin da ke faruwa a yanzu ba.”

Aminiya ta tuntuni Jami’in Hulda da Jama’a na Rundunar ’Yan Sandan Jihar Yobe, ASP Dungus Abdulkarim, wanda ya shaida wa wakilinmu cewa kokarin sanin hakikanin halin da ake ciki a garin na Geidam, da zarar sun tabbatar da hakikanin bin da ya faru zai sanar.

Garin na Geidam dai yana gab ne da kan iyaka da garin Maine Sarua na Jumhuriyar Nijar, inda akan fuskanci hare-haren mayakan Boko Haram.

Irin wannan lamarin dai kan sa al’ummar garin guje-guje domin tsira da rayukansu.