✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Ya kashe wanda yake zargin na badala da matarsa

Wani mutum mai shekaru 35 mai suna Habeeb Kasali, ya shiga komar ‘yan sandan jihar Ogun bisa zargin da ake masa na kashe wani mutum…

Wani mutum mai shekaru 35 mai suna Habeeb Kasali, ya shiga komar ‘yan sandan jihar Ogun bisa zargin da ake masa na kashe wani mutum mai suna Bamidele Johnson, wanda ya ce yana badala da matarsa.

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Ogun DSP Abimbola Oyeyemi, ya shaidawa Aminiya cewa jami’an sun kame mutumin wanda ya tsere bayan ya aikata aika-aikar,” ‘Yan uwan mamacin sun shigar da maganar ga rundunar ‘yan sanda, inda suka ce fada ne ya barke a tsakanin wanda ake zargin da mamacin mai shekaru 32, wanda ake zargi da kisan ya hau shi da fada yana fada masa cewa, yana badala ta matarsa duk da cewa a baya ya yi masa kashedi ba sau daya ba, ba sau biyu ba, daga nan ya sanya almakashi ya soki mamacin a kirji da ido da wasu sassan jikinsa, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwarsa a asibitin Crest da ke yankin Egan a Legas.” In ji shi.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Ogun CP Kenneth Ebrimson, ya bada umarnin tura wanda ake zargin sashin binciken manyan laifuka na rundunar domin ci gaba da bincike a yayin da ake ajiye da gawar mamacin a dakin ajiyar gawa na babban asibitin Sango Ota a Jihar Ogun.