An gudanar da jana’izar sojojin rundunar da ke tsaron shugaban kasa da ’yan bindiga suka kashe a wani hari a yankin Bwari da ke Abuja.
A ranar Alhamis aka kai sojojin su hudu makwancinsu a Makabartar Sojoji da ke Maitama a Abuja.
- Ya yi garkuwa da ma’aikatan banki kan hana shi cire kudinsa
- Fafaroma Bai Hana Ni Yi Wa Musulmi Yakin Neman Zabe Ba —Lalong
Tun da farko sai da aka gudanar addu’o’i a Cocin Sojoji na St. Johns kafin a kai su makabartar.
Sojojin, ciki har da hafsoshi hudu, sun kwanta dama ne bayan harin da ’yan bindiga suka kai musu a lokacin da suke dawowa da sintirin dakile harin da ’yan bindiga ke shirin kaiwa a Makarantar Koyon Aikin Lauywa da ke Bwari, Abuja.
A jawabansu na ta’aziyya, Kwamandojojin rundunonin, Laftanar Kanar Salim Yusuf Hassan da Laftanar Kanar Joshua Kolawole Adisa, sun bayyana marigayan a matsayin jarumai abin koyi wajne kare kasarsu.