✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Yadda ake bude makarantun kudi a Kwara abin damuwa ne – Majalisa

Majalisar ta ce ba a cika ka’idar bude makarantun a jihar

Duba da yadda ake samun karuwar bude makarantu masu zaman kansu a jihar Kwara, Majalisar Dokokin Jihar ta yi kira da a tsananta bin dokokin kafa makarantun a jihar.

Majalisar ta nuna damuwarta kan tumbatsar makarantun kudi da ake samu a jihar, wanda a cewarta hakan zai iya yin illa ga ingancin ilimi a jihar.

Da yake mika korafinsa kan batun yayin zaman majalisar a ranar Talata, Honarabul Abdullahi Danbaba na jam’iyyar APC, ya ce, rashin aiki ya sa matasa da suka kammala karatu a jihar suka shiga bude makarantu ba tare da cika ka’idoji ba.

Ya ce akwai bukatar Ma’aikatar Ilimi ta jihar ta dada matsa kaimi wajen tabbatar da ana cika sharuddan da aka gindaya kafin bude makarantun.

Korafin na Danbaba ya samu goyon bayan takwarorinsa a majalisar inda da yawansu suka ce dole gwamnati ta sa ido a kan batun don gudun gurbacewar ilimi a jihar.

Shugaban Majalisar, Honarabul Yakubu Salihu, ya bukaci Ma’aikatar Ilimin jihar ta tabbatar da ana kiyaye ka’idojin da aka shimfida kafin bude makarantun.

(NAN)