✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Yadda ’yan Burkina Faso ke murnar juyin mulkin da aka yi

Dubban mutane na jin dadin yadda aka hambarar da gwamnatin Shugaba Kabore.

Magoya bayan sojojin da suka yi juyin mulki a kasar Burkina Faso sun gudanar da gangamin nuna goyon baya kan hambarar da gwamnatin kasar.

Al’ummar kasar na murnar juyin mulkin ne a daidai lokacin da Kungiyar Bunkasa Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) da Majalisar Dinkin Duniya suke la’antar juyin mulkin.

Dubban magoya bayan sojojin ne suka fito kan titunan Ouagadougou, fadar gwamnatin kasar, dauke da tutar kasar suna bushe-bushen sarewa a yayin gangamin nasu na nuna goyon baya ga sojojin da suka kifar da gwamantin Shugaba Roch Christian Marc Kabore.

Daya daga cikin masu shirya gangamin, Lassane Ouedrago, ya ce sun dade suna kira ga Shugaba Kabore da ya sauka daga kujerarsa saboda gazawarsa wajen magance kashe-kashen da ake yi a cikin kasar amma ya yi kunnen uwar shegu.

A ranar Litinin ne, dakarun sojin Burkina Faso suka kame Shugaba Christian Kabore, wanda jama’ar kasar suka sha yi wa zanga-zanga a kan gazawarsa wajen dakile hare-haren ’yan ta’adda a kasar.

A halin yanzu dai kasar na hannun Laftanar-Kanar Paul-Henri Sandaogo Damiba wanda shi ne ya jagorancin hambarar da Gwamnatin Kabore, sannan ya sa aka tsare shi.