✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Yadda za a karrama zakarun Gasar Gajerun Labarai ta Aminiya-Trust

Za a karrama gwarazan shekara da wasu ’yan takara na gasar Aminiya-Trust ta 2020.

A ranar Asabar 5 ga Yuni, 2021 ake sa ran gudanar da bikin mika kyaututtuka ga gwarazan Gasar Rubutun Gajerun Labarai ta Aminiya-Trust ta 2020 a birnin Kaduna.

Tuni dai alkalai suka tantance rubutu da marubuta uku da za a zabi na daya zuwa na uku daga cikinsu don lashe gasar.

Jagoran gasar, Farfesa Ibrahim Malumfashi ya fadi a wata sanarwa cewa an tsamo mutum uku a matsayin wadanda suka kasance gwarazan gasar ta 2020 don karrama su a ranar.

Kuma ya ce akwai ’yan takara 12 da su ma za a yaba wa kwazonsu a yayin taron wajen ba su kyaututtuka.

 

Zakarun Gasar Rubutu ta Aminiya-Trust ta 2020

Sunayen gwarazan da rubutunsu suka samu nasara da za a zabi na daya zuwa na uku sun hada da:

Dimokuradiyyar talaka, na Rufaida Umar Ibrahim.

Ranar kin dillanci, na Ubaida Usman

Tufka da warwara, na Mubarak Idris Abubakar

 

’Yan takara 12 da za a yaba wa kwazonsu a yayin taron su ne:

  1. Komai nisan dare. Na Yaseer Kallah
  2. Hassada ga mai rabo. Na Mustapha Sufyanu Jikan Malam
  3. Baki guba ne. Na Basira Sabo Nadabo
  4. Tsaka mai wuya. Na Salim Yunusa
  5. Kawalweniya. Na Mujaheed Ameen Lilo
  6. Kazar kwanci. Na Maryam Umar Sakkwato
  7. Ci ga rashi. Na Isma’il Gambo
  8. Igiyar Linkaya. Na Hajara Ahmed Hussaini.

Yadda bikin zai gudana

Za a gudanar da bikin ne a Hotel 17 da ke garin Kaduna da misalin karfe 7:00 na dare insha Allah.

Sai dai kuma wadanda aka gayyata ne kawai za a bari su shiga harabar bikin, wadanda su ma dole ne su zo da takunkumi tare da kiyaye ka’idojin yaki da cutar COVID-19.