✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

’Yan bindiga daga Zamfara da Katsina sun fara kai hari Kano

’Yan bindigar sun fara kai hari suna garkuwa da mutane a Rogo.

Hare-haren da sojoji suke kai wa ’yan bindiga a jihohin Katsina da Zamfara sun tilasta musu tserewa zuwa Jihar Kano da ma wasu jihohin. 

Dan Majalisar Tarayya mai wakiltar Rogo da Karaye a Majaliar Wakilai, Haruna Isah Dederi, ya ce a kwanakin baya ’yan bindiga sun kai hare-hare gami da garkuwa da mutane garuwa bakwai a Karamar Hukumar Rogo ta Jihar Kano.

Ya ce garuruwan ’yan bindiga suk yi garkuwa da mutane a yankin sun hada da garin Jajaye, Zarewa, Ruwan Bago, Bari, Falgore, Dutsen Ban da Hawan-Gwamna (Fulatan).

“Idan ba a gaggauta daukar matakai ba na hana yaduwar ’yan bindigar a Karamar Hukumar Rogo da wasu kananan hukumomin Jihar Kano musamman wadanda ke kan iyaka, matsalar na iya yaduwa zuwa wasu kananan hukumomi tare da gurgunta amincin da ake da shi a jihar Kani,” inji dan Honorabul Dederi.

Ya yi kuma yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta kara tsanantawa wajen ragargazar da take wa ’yan bindiga a jihohin Zamfara da Katsina ta hanyar fadada matakan zuwa wasu wurare.

A cewarsa, yin hakan na da muhimmanci a sauran yankunan da matslar ta shafa domin gudanar da hare-haren a lokaci guda zai hana bata-garin samun sukunin tserewa zuwa wasu wuraren.