✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

’Yan bindiga sun huce fushi kan masu ba wa jami’an tsaro hadin kai

Wannan hukunci ne a sakamakon bai wa jami’an tsaro bayanai a kansu da suke yi.

’Yan bindiga sun kashe wasu mutane biyar mazauna garin Rogoji da ke Karamar Hukumar Bakura ta Jihar Zamfara a wani hari da suka kai a karshen wannan mako.

Da suke tabbatar da wannan al’amari, mazauna yankin sun ce ’yan bindigar sun yi musu aika aikar ne a matsayin hukunci, sakamakon bai wa jami’an tsaro bayanai a kansu da suke yi.

RFI ya ruwaito cewa garin Rogoji na da nisan kilomita 2 ne kawai daga kwaryar garin Bakura.

Majiyoyi sun ce mazauna garin sun taimaka wa jami’an tsaro da ‘yan banga sosai a wajen yaki da ‘yan ta’addan da suka hana su sakat a yankunan Lambar Bakura da Dogon Karfe.

Bayanai sun ce ’yan bindigar sun shiga garin ne da safiyar Alhamis a lokacin da al’umma ke shirin sallar asuba, duk da turjiya da suka gamu da ita, inda suka kashe mutane 5.