✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

’Yan bindiga sun kashe mutum 15 a Sakkwato

Tambuwal ya mika ta’aziyyarsa ga ’yan uwan wadanda suka mutu.

Kimanin mutum 15 ne ake fargabar sun mutu a wani hari na ranar Lahadi da ’yan bindiga suka kai Kananan Hukumomi Goronyo da Illela na Jihar Sakkwato.

Gwamnan Jihar, Aminu Waziri Tambuwal wanda ya tabbatar da hakan a ranar Litinin, ya ce mutum 12 aka kashe a Illela yayin da kuma ragowar ukun suka rasa rayukansu a Goronyo.

Gwamna Tambuwal ya bayyana haka ne jim kadan gabanin gabatar da Kasafin Kudin Jihar Sakkwato na shekarar 2022 a gaban Majalisar Dokokin jihar.

Tambuwal hare-haren sun auku ne a tsakanin daren Lahadi zuwa wayewar gari na Litinin a Kananan Hukumomin da lamarin ya shafa.

Gwamnan ya kuma mika ta’aziyyarsa ga ’yan uwan wadanda suka mutu da kuma wadanda suka jikkata a hare-haren.

Bayanai sun ce Kananan Hukumomin biyu da lamarin ya shafa na daga cikin wadanda gwamnati ta bayar da umarnin katse musu layukan sadarwa a yunkurinta na kawo karshen matsalar tsaro a Jihar.

Duk wannan dai na faruwa ne a yayin da wasu rahotanni ke cewa yan bindiga sun fara daula a kauyuka da dama na Jihar Sakkwato inda har sun shata wa mazauna haraji.