✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

’Yan bindiga sun kashe mutum 20 a kauyukan Kaduna

Maharan sun banka wa gidaje da motoci da amfanin gona wuta a wasu kauyuka uku.

’Yan bindiga sun kashe akalla mutum 20 a Karamar Hukumar Giwa ta Jihar Kaduna.

Maharan sun rika banka wa gidaje da motoci da amfanin gona a gonaki wuta a wasu kauyuka uku.

Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na Jihar Kaduna, Samuel Aruwan, ya tabbatar da harin a ranar Lahadi.

Ya ce an kai hare-haren ne a kauyukan Kauran Fawa da Marke da kuma Riheya da ke yankin Idasu.

Aruwan ya bayyana ta’aziyyar Gwamnan Jihar, Nasir El-Rufai ga iyalan mamatan tare da umartar Hukumar Ba Da Agaji ta Jihar ta kai musu tallafi.