✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

’Yan bindiga sun kashe ’yan sanda 4 a Kebbi

’Yan bindiga akalla 500 sun kai hari wani kamfanin tumatir suna yunkurin sace shugabannin kamfanin.

’Yan bindiga sun kashe ’yan sanda hudu da wani farar hula a kamfanin tumatir na GBFoods Africa da ke kauyen Gafara a Karamar Hukumar Ngaski ta Jihar Kebbi.

Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kebbi, DSP Nafiu Abubakar, ya ce mutanen da suka samu raunin harbi a harin ba za su kirgu ba, domin ’yan bindiga kusan 500 ne suka yi wa kauyen da kamfanin kawanya, aka yi musayar wuta tsakaninsu da jami’an tsaro.

“’Yan bindiga akalla 500 ne suka kai hari kamfanin tumatir din da ke kauyen Wawu a Karamar Hukumar Ngaski, suka yi yunkurin sace shugabannin kamfanin.

“’Yan sanda hudu da wani mutumin kauyen sun rasa rayukansu sakamakon musayar wuta da aka yi a tsakaninsu da maharan,” inji shi.

A cewarsa, ’yan bindigar sun shiga kamfanin ne suna neman shugabannin kamfanin, sai dai an yi dauki-ba-dadi tsakaninsu da jami’an tsaro wanda a sanadiyar haka aka jikkata mutane da dama daga kowane bangare.

Ya ce wadanda suka ji rauni ba za su lissafu ba amma an kai wani asibiti wanda ba a bayyana sunansa ba ana ba su agajin gaggawa, yayin da su kuma ’yan bindigar suka kwashe gawarwakin ’yan uwansu.

Kakakin ya bayyana cewa an jibge karin ’yan sanda a yankin don tabbatar da komai ya daidaita.