✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

’Yan bindiga sun mayar da mata 22,000 zawarawa a Zamfara

Yara 44,000 sun zama marayu bayan an kashe magidanta sama da 11,000 a Zamfara

Kimanin mata dubu 22 ne ’yan bindiga suka yi wa mazajensu kisan gilla a Jihar Zamfara.

Kungiyar matasan Arewa ta AYF ce ta sanar da haka inda ta kara da cewa baya ga zawarawan, hare-haren ’yan bindigar ya mayar kananan yara dubu 44 marayu a jihar.

“Yana da wahala a yi kwana guda ba tare da an samu irin wannan aika-aikatar ba a yanzu”, inji Shugaban AYF, Gambo Ibrahim Gujungu.

Ya ce kimanin magidanta dubu 11 ne ’yan bindiga suka hallaka a cikin shekara takwas da jihar ta yi fama da matsalar ’yan fashin daji da sauran miyagu.

Gujungu ya nuna damuwa game da barnar ’yan bindiga da suka hada da kashe-kashe, satar dabbobi, fyade, garkuwa da kuma mutane a jihar da kuma yankin Arewa maso Yamma.

Ya bukaci a gaggauta daukar matakan magance matsalolin da ya ce na iya haifar da mummunan sakamako muddin aka ci gaba da zura ido ba tare da daukar matakan da suka dace ba.

Yankin Arewa maso Yamma wanda a can baya ya kasance mai zaman lafiya da aminci na fama da matsalolin tsaro da suka yi ajalin dubban mutane da tilasta wa wasu gudun hijira.

Baya ga irin asarar das matsalar da ta ki ci ta ki cinyewa ta jawo, ta kuma jefa al’ummomi cikin fargaba musamman yankunan karkara inda manoma ba sa iya noma gonakinsu.