✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

’Yan Boko ne matsalar Najeriya —Sarkin Musulmi

Rashin shugabanni na gari zai tarwatsa duk wani hadin kai a tsakanin al'umma.

Shugaban Majalisar Koli ta Harkokin Addinin Musulunci a Najeriya, Mai Alfarma Sarkin Musulmi ya bayyana cewa ’yan boko da masu fada aji a kasar nan su ne matsalar Najeriya.

Alhaji Sa’ad Abubakar ya fadi hakan ne a yayin wani taron wanzar da zaman lafiya da gina kasa da Kwamitin Shirya Da’awah na Kasa ya shirya karo na uku a Jihar Gombe.

Wakilinmu ya ruwaito cewa, a yayin taron ne kwamitin wanda ya hada mabiya addinin Kirista da Musulmi ya tattauna matsalolin da ke hana ruwa gudu wajen samun zaman lafiya a kasar nan.

A jawabinsa, Sarkin Musulmi ya kalubalanci shugabannin da cewa su koma wa littatafan su masu tsarki don samun ginshikin shugabanci na gari.

A cewarsa, muddin aka rasa kyakkyawan shugabanci to za a rasa zaman lafiya da hakan zai tarwatsa duk wani hadin kai a tsakanin al’umma.

Aminiya ta ruwaito cewa, kafin taron ne Sarkin Musulmin ya jagoranci bude wata hanya a garin Gombe da Gwamna Muhammad Inuwa Yahaya ya gina kuma aka sanya mata sunansa a Unguwar Gandu.