✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

‘Yan fashi sun kashe ‘yan sanda a motar kudi

‘Yan fashi sun kai wa motar daukar kudi hari suka kashe ‘yan sanda hudu da ke rakiyar kudin zuwa birnin Abakiliki, Jihar Ebonyi. Abun ya…

‘Yan fashi sun kai wa motar daukar kudi hari suka kashe ‘yan sanda hudu da ke rakiyar kudin zuwa birnin Abakiliki, Jihar Ebonyi.

Abun ya faru ne a mahadar hanya da ke garin Ezzemgbo na Karamar Hukumar Ohaukwu.

Wata majiya ta ce, ‘yan fashin sun tare motar ce a kan hanyarta na kai kudi wani banki da ke titin Ogoja a birnin Abakiliki.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Philip Maku ya tabbatar da cewar ‘yan fashin sun biyo motar ne daga Inugu.

Ya kara da cewa ‘yan fashin ba su dauki kudin ba saboda direban ya tsere musu.

“Sun fasa tayar motar daukar kudin daya amma direban ya tsere da motar da kudin. Sun kasa bin motar ne saboda driver ya tunkari sansanin sojoji”.

Kwamishinan ya ce, ‘yan sanda biyu da suka ji ciwo an kai su Asibiti. Sai kuma gawarwakinsu a mucuwari.

Ya kuma ce ‘yan sanda sun bazama nema ‘yan fashin.