Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta ce fiye da ’yan Najeriya 30,000 ne ke mutuwa duk shekara a sanadiyar cututtukan da ke da alaka da shan taba sigari.
WHO ta bakin wakilinta Walter Mulombo ta bayyana cewa adadin ya ninka na mutum 3,144 da cutar COVID-19 ta kashe a Najeriya.
- ’Yan bindiga sun fara harbin fasinjojin jirgin kasan da ke hannunsu
- Mahara sun kashe jami’an tsaro sun sace mutane a Kaduna
Ya bayyana haka ne yayin kaddamar da manhajar adana bayanan tsare-tsaren yaki da shan sigarin A Najeriya, wadda Kamfanin IREX da hadin guiwar Ma’aikatar Lafiya ta Tarayya suka samar, a bikin Ranar Yaki da Shan Sigari ta Duniya, ranar Talata.
A nasa bangaren, Ministan Lafiya, Adeleke Mamora, ya ja hankalain ’yan Najeriya da su guji shan sigari ko zama a inda ake sha, domin hakan ya fi illa ga lafiyar jikin dan Adam kamar yadda masana kiwon lafiya ke fada.
Minitsan ya kuma ce tun daga ranar 1-6-2022, Najeriya ta fara amfani da sabon tsarin biyan harajin taba sigari na shekara uku da zai kare a shekara ta 2024.