✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

’Yan sanda sun ceto dan shekara 50 da aka sace a Jigawa

'Yan sandan sun yi wa maharan kwanton bauna.

’Yan Sandan a Jigawa ta ceto wani mutum mai shekara 50 da aka yi garkuwa da shi, Musa Barma, a Karamar Hukumar Malam-Madori.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da kakakin ’yan sandan jihar, DSP Lawan Shiisu Adam, ya fitar ranar Talata.

Ya ce lamarin ya faru ne a ranar Asabar da misalin karfe 2:30 na rana, inda wasu ’yan bindiga suka kai farmaki gidan Musa Barma suka yi awon gaba da shi.

Ya ce bayan samun labarin, ’yan sandan sun gano su, suka yi musu kwanton bauna a kan hanyar da ’yan bindigar suka bi a kusa da kauyen Arbus a Karamar Hukumar Kaugama.

Ya bayyana cewa, sakamakon musayar wuta da ’yan bindigar, ‘yan sanda, sun yi nasarar ceto wanda aka yi garkuwa da shi ba tare da ya ji rauni ba, yayin da maharan suka tsere zuwa cikin daji.

Shiisu, ya ce an kama mutum daya mai suna Nura Ahmad a unguwar Abuja a Karamar Hukumar Malam Madori wanda ake gudanar da bincike a kansa.

Ya ce an mayar da binciken lamarin zuwa hedikwatar SCIID domin gudanar da bincike mai zurfi.