✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

’Yan sanda sun kama magoya bayan Arsenal kan murnar doke United

’Yan sanda sun ce magoya bayan na Arsenal ba su da izinin gudanar da gangamin.

Wani abun al’ajabi ya faru a kasar Uganda inda jami’an tsaro suka rika bi suna cafke magoya bayan kungiyar kwallon kafa ta Arsenal.

BBC ya ruwaito cewa, akalla magoya bayan Arsenal takwas aka kama a birnin Jinja na kasar, sakamakon murnar nasarar da kungiyar ta yi kan babbar abokiyar hamayyarta Manchester United a wasan Firimiyar Ingila da suka buga ranar Lahadi.

Magoya bayan – wadanda ke sanye da jajayen rigunan kungiyar – na rike da wani abu da ke alamta kofin Firimiyar.

’Yan sanda sun ce mutanen ba su da izinin gudanar da gangamin, kuma yin hakan laifi ne a kasar.

’Yan sanda sun kama magoya bayan – wadanda ke cikin jerin gwanon motoci ranar Litinin da safe – inda daya daga cikinsu ke rike da kofin da suka hada kudi suka saya a wani shago a kasar.

Arsenal dai ta samu nasara a kan abokiyar hamayyarta Manchester United da ci 3-2 a wasan na ranar lahadi.

Sakamakon ya bai wa kungiyar tazarar maki biyar a saman teburin Firimiyar Ingila, lamarin da ya bai wa magoya bayanta a fadin duniya kwarin gwiwar daukar kofin karon farko cikin shekara 19.