✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

‘Yan sanda sun kama ‘yan bindiga 5 a Jigawa

An cafke 'yan bindigar tsakanin Jigawa da Kano.

Rundunar ‘yan sanda a Jihar Jigawa ta yi nasarar cafke wasu mutum biyar da ake zargin ‘yan bindiga ne da kuma aikata fashi da makami a Karamar Hukumar Ringim ta jihar.

Kakakin ‘yan sandan Jihar, ASP Lawan Shiisu ne ya tabbatar da hakan yayin zantawa da Kamfanin Dillacin Labarai (NAN) ranar Litinin a Dutse, babban birnin Jihar.

“Wadanda ake zargin na da hannu a aikata fashi da makami da kuma garkuwa da mutane tsakanin jihohin Jigawa da Kano.”

Shiisu ya ce wanda ake zargin da farko sun nuna sha’awar mika wuya ga jami’an tsaro.

Ya kara da cewa jami’an ‘yan sandan sun yi samame tare da kame wani mai shekara 30 a Karamar Hukumar Ajingi da ke Jihar Kano.

Ragowar kuma sun shiga hannun ne a garuruwa daban-daban tsakanin Kano da Jigawa tun a ranar 26 ga wata Maris.

Ya ce a halin yanzu ababen zargin na ba da hadin kai wajen binciken da ake gudanarwa.

Shiisu ya ce za a mika su zuwa kotu da zarar an kammala bincike a kansu.