✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

’Yan sanda sun kwato shanu 275 daga ’yan bindigar Kaduna

’Yan sandan sun yi nasarar kwato shanu daga hannu ’yan bindiga a Jihar Kaduna. 

’Yan sandan sun yi nasarar kwato daruruwan shanu daga hannun ’yan bindiga a Jihar Kaduna.

Jami’in Hulda da Jama’a na Rundunar ’Yan Sandan Jihar, ASP Mohammed Jalige, ya ce jami’ansu da ke yin sintiri a yankin sun yi kwato shanu 137 daga hannun ’yan bindigar a yankin Zariya.

“A ranar 29 ga Afrilun 2021, jami’an ’yan sanda sun kwato shanu 137 cikin shanu 138 da ake nema, kuma tuni aka mayar wa da masu shanun dabbobinsu,” a cewarsa.

Ya ce, ranar 20 ga watan Afrilun kuma, Rundunar ta rahoto daga jami’inta mai kula da yankin Afaka kan yadda makiyaya ke gudanar da harkokinsu a yankin.

“An yi nasarar karbe shanu 138 daga hannun wasu ’yan bindiga inda aka kama su za su yi awon gaba da su.

“Ba mu yi kasa a gwiwa ba sai da muka tabbatar an karbe shanun.

Jalige ya ce, ’yan bindigar guda biyun da aka kama har yanzu ana gudanar da bincike a kansu.

“Muna iya bakin kokarinmu na tabbatar an kubutar da mutanen da aka yi garkuwa da su,” inji shi.